GANIN WATA


Kamar yadda dai ka sani ne cewa yanayin jinjirin wata a karshensa (ko kuma a farkonsa) ba ya fita daga daya daga cikin wadannan halaye:
(1) Buyan wata ya kasance kafin faduwar rana.
(2) Buyan wata ya kasance dai-dai da faduwar rana.
(3) Buyan wata ya kasance bayan faduwar rana.
To muna so ayi mana bayanin wadannan al'amura:
Na farko: A cikin wadannan halaye guda uku, a mahangan fikhu wanne ne a ke daukansa farkon wata.
Na biyu Idan muka yi la'akari da cewa dukkan wadannan halaye guda uku a kan iya gano su ta hanyar naurori da suke yin wannan aiki to shin ana iya amfani da wannan na'ura wajen gano farkon wata, ko kuma dai wajibi ne sai an gan shi da ido?
Abin la'akari dangane da farkon wata shi ne watan da yake buya bayan faduwar rana, wanda za'a iya ganin sa kafin faduwar rana ta yadda aka saba.
Idan aka samu sabani tsakanin maluman wani gari dangane da ganin wata da kuma rashin ganin sa, kuma adalcin wadannan malamai dukkansu ya tabbata ga mutum, kuma yana da yakini kan bincike da bin diddigin kowane daya daga cikinsu, to mene ne ya wajaba ya aikata?
Idan har wannan sabani nasu kan korewa ne da kuma tabbatar (da ganin watan) kamar wasunsu su yi da'awar tabbatar watan kana wasu kuma su yi daawar tabbabar da rashin tsayuwarsa, to hakan karo ne tsakanin hujjojin guda biyu, to a wannan hali sai mutum ya jefar da dukkan wadannan maganganu biyu, ya koma ya yi riko da abin da shari 'a ta tabbatar na yin aiki da asali daga usul, wato kamar babu wadannan maganganu, to amma da sabanin nasu ya ta'allaka ne da tabbatarwa da kuma rashin masaniya kan tabbatuwan, kamar wasunsu su yi da'awar ganinsa wasu kuwa su ce su ba su gan shi ba, to maganar wadanda suka ce sun gani idan dai adilai ne shi ne abin riko a shar'ance ga mutum kuma, wajibi ne ya bi hakan, haka kuma da marja'i ko kuma waliyul fakih zai bayar da sanarwar ganin watan, to hukuncinsa hujja ce ga dukkan mutane, kuma wajibi ne su bi shi.
Wasu hanyoyi ne ake bi wajen gano watan Ramalana da kuma daren idi? Shin ya inganta a dogara ga kalanda?
Hakan yana tabbata ne da ganin shi kansa mukallafi ga watan, ko kuma shaidar mutane biyu adalai, ko kuma yaduwan labarin ganin watan tsakanin al'umma, ta yadda mutum ya sami ilimi ta haka ko kuma da cikan watan kwana talatin, ko kuma da hukuncin marja'i ko waliyul fakih.
Da ace ya halatta a bi abin da wata hukuma ta sanar dangane da ganin wata, kuma wannan sanarwa ya kasance wani mizani na tabbatuwan ganin wata a wasu garuruwan, to shin wajibi ne wannan hukuma ta zama ta musulunci, ko kuma za'a iya amfani da hakan ko da kuwa hukuncin ya fito ne daga hukuma azzaluma fajira?
Abin la'akari kawai shi ne samuwar nitsuwa kan ganin watan a wannan guri.