MAS'ALOLI DABAN-DABAN KAN AZUMI


Mene ne hukuncin macen da jinin haila ya zo mata yayin da take azumin bakance mai takamammen lokacin yinsa wato ayyananne?
Daga fitowar jinin azumin nata yakan baci, to amma wajibi ne ta rama shi bayan ta sami tsarki.
Mutum ne yake zaune a wani gari to sai ya yi azumi tun daga farko har zuwa rana ta ashirin da bakwai na wannan wata mai alfarma, to ran ashirin da takwas na wannan wata sai ya yi tafiya zuwa wata kasa inda ya isa ran ashirin da tara, sai ya samu sun sanar da ganin wata, to daga nan sai ya koma kasarsu, to shin wajibi ne ya rama abin da ya tsere masa na daga azumin?
Idan ya rama rana guda, to watan Ramalana zai kasance kwana ashirin da takwas kenan a gare shi, idan kuma ya ce zai rama kwanaki biyu ne, to ai a ranan 29 na wannan wata yana garin da suka riga suka sanar da ganin wata ne, to a nan mene ne hukuncin wannan mutum?
Idan har wannan sanarwa na ganin wata ran 29 a wancan kasa da ya je dai- dai ne a mahangan shari a, to ramakon azumin wannan rana a gare shi ba wajibi ba ne, sai dai hakan yana tabbatar da kubucewar daya azumin gare shi a farkon watan, dan haka wajibi ne ya rama abin da ya tsere masa bisa yakini na daga azumin.
Da mutum zai sha ruwa bayan faduwar rana a wani gari, to sai ya tafi wani garin da su a gurinsu rana ba ta fadi ba, to mene ne hukuncin azuminsa na wannan rana? Kana shin zai iya ci gaba da cin abincinsa a wannan garin kafin faduwar ranarsu?
Azuminsa ya inganta kuma zai iya ci gaba da cin abincinsa kafin faduwar rana a wannan garin.
Mu kan ji daga bakin wasu maluma cewa idan aka gayyaci mutum ga walimar cin abinci alhali kuwa yana azumi na mustahabi, zai iya cin wannan abinci kuma hakan bai bata masa azuminsa ba, to a nan muna so mu ji fatawarka kan hakan.
Amsa gayyatar mumini zuwa ga cin abinci yayin azumin mustahabi, al'amari ne da a ka so shi a sharia, cin abincin muminin da ya gayyaci dan ' uwansa mumini ko da yake yana bata azumi, to amma ba ya hana samun ladansa.